Pages

Games

Friday 21 July 2017

Labari kasa daga fadar shugaban kasa

Shekaru biyu da hawan shugaba Buhari mulki, ya fara samun suka da soyayya kan batun 2019

- Ana jinyar shugaba Buhari kusan duk shekarar nan

- Fadar Shugaban kasa tace shine ma zai lashe zabe kuma zayyi takara

Mataimakin Shugaba Buhari kan harkokin manema labarai, Malam Garba Shehu, yace ko da a yau aka gudanar da zaben shugaban kasa, toh lallai Buhari ne zai lashe zaben, domin a cewarsa, 'yan Najeriya na farin ciki da yadda salon mulkin Buharin yake. Ya dai fadi hakan ne, a yau da safe a gaban manema labarai.

Www.bestarewa.com.ng

Shugaban kasa Muhammadu Buhari

Malam Garba Shehun, ya kara da cewa, ai ma duk soki-burutsu ne na siyasa jam'iyyar adawa take yi, domin kayen da suka sha a shekaru biyu da suka gabata a shekarar 2015.
For more visit www.bestarewa.com
An dai shafe shekaru biyu kenan tun da jam'iyyar APC ta amshi mulki, kuma shugaba Buhari na jinya a asibiti a Turai, kusan duk tsawon wannan shekara, bai kuma ce zayyi ko bazai yi takara ba a zabe mai zuwa.

No comments

Post a Comment

Designed With & By Abijah Johnnie
Designed With & By Abijah Johnnie