Pages

Games

Tuesday 22 August 2017

[LABARI DUNIYA] Yan Sanda sun damke Dan Indiya yana mummunan laifi a Najeriya

An kama wani Dan Kasar Indiya yana ta'adi a Najeriya

- An samu wannan mutumi yana saida rubabbun magunguna

- Sai dai har yanzu ba a san sunan wannan mai laifi ba

'Yan Sanda sun kama Dan wata kasa yana ta'adi a Najeriya wanda hakan na iya kai ga daure sa don ya aikata babban laifi.


An kama wani yana ta'adi a Najeriya

An samu wannan mutumi Dan kasar Indiya yana saida rubabbun magunguna da su ka lalace a sababbin kwali. Kamar yadda labari ya zo mana dai daga Channels TV har yanzu ba a san sunan wannan babban mai laifi ba.

An kama masu saida rubabbun kwayoyi a Kano

Wannan mutumi ya kan maida magungunan da aikin su ya kare zuwa cikin kwali ya saida kamar na yau. Hukumar NAFDAC dai tana yaki da wannan laifi a Kasar. Wannan abu ya faru ne a Nasarawa a Jihar Kano.

Dama dai ana kukan cewa Hukumar NAFDAC din tayi barci a Kasar. Wannan na zuwa ne bayan Inyamurai sun yi wani taro inda su kace shirya karbar mulkin Kasar nan a zabe mai zuwa inda su kace su ne su ka fi dadewa da Mulkin.

No comments

Post a Comment

Designed With & By Abijah Johnnie
Designed With & By Abijah Johnnie